WAƘA TA 80
‘Mu Dandana, Mu Gani, Ubangiji Nagari Ne’
(Zabura 34:8)
-
1. Muna daraja bautarmu
Da wa’azin da muke yi.
Muna wa’azi da duk ƙarfinmu
Don kowa ya ji saƙonmu.
(AMSHI)
Jehobah ya ce: ‘Mu ɗanɗana
Mu ga duk alherinsa.’
Mu bauta masa da ƙarfinmu,
Zai yi mana albarka.
-
2. Majagaba ʼyan’uwanmu,
Jehobah zai ƙarfafa ku.
Zai kuma biya duk bukatunku,
Ba zai yi watsi da ku ba.
(AMSHI)
Jehobah ya ce: ‘Mu ɗanɗana
Mu ga duk alherinsa.’
Mu bauta masa da ƙarfinmu,
Zai yi mana albarka.
(Ka kuma duba Mar. 14:8; Luk. 21:2; 1 Tim. 1:12; 6:6.)