WAƘA TA 98
Nassosi Hurarre Ne Daga Allah
(2 Timotawus 3:16, 17)
-
1. Kalmar Allah na taimaka,
Tana sa mu ga haske.
In muna bin umurninta,
Za mu ceci rayukanmu.
-
2. Ya yi tanadin Kalmarsa,
Don mu san umurninsa.
Tana ƙarfafa mutane,
Tana horar da mu sosai.
-
3. Kalmar Allah ta sa mu san,
Cewa Yana da ƙauna.
Karanta ta a koyaushe
Zai sa mu riƙe aminci.
(Ka kuma duba Zab. 119:105; Mis. 4:13.)