WAƘA TA 74
Mu Rera Wakar Mulkin Allah!
(Zabura 98:1)
-
1. Ku zo mu yi wannan sabuwar waƙa,
Waƙar na ɗaukaka Maɗaukaki.
Kalmomin waƙar na da ban ƙarfafa.
Waƙar tana ƙarfafa mu cewa:
(AMSHI)
‘Mu bauta wa Maɗaukaki!
Ɗansa shi ne Sarkin Mulkin.
Sai ku zo don mu koyi waƙar Mulkin,
Mu ɗaukaka Allah da sunansa.’
-
2. Da waƙar nan muke shelar Mulkinsa.
Yesu Kristi ne zai yi sarauta
Kuma akwai waɗansu mutane ma
Da za su yi sarauta da Yesu:
(AMSHI)
‘Mu bauta wa Maɗaukaki!
Ɗansa shi ne Sarkin Mulkin.
Sai ku zo don mu koyi waƙar Mulkin,
Mu ɗaukaka Allah da sunansa.’
-
3. Amintattu ne suke rera waƙar,
Kalmominta da sauƙin rerawa.
A duniya mutane sun koye ta,
Suna yi wa wasu shelar waƙar:
(AMSHI)
‘Mu bauta wa Maɗaukaki!
Ɗansa shi ne Sarkin Mulkin.
Sai ku zo don mu koyi waƙar Mulkin,
Mu ɗaukaka Allah da sunansa.’
(Ka kuma duba Zab. 95:6; 1 Bit. 2:9, 10; R. Yoh. 12:10.)