Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 132

Yanzu Mun Zama Daya

Yanzu Mun Zama Daya

(Farawa 2:​23, 24)

  1. 1. A ƙarshe ga kamanina,

    Da jikina, ina godiya.

    Allah ya ba ni mai so na

    Da mataimakiya.

    Yau mun zama iyali fa,

    Za mu riƙa samun albarka.

    Za mu bauta wa Jehobah

    Don shi ne Allahnmu.

    Kalmarsa na taimaka mana,

    Kalmar tana sa

    Mu riƙa ƙaunar juna.

    Wa’adi ne, za mu cika,

    Hakan zai sa mu riƙa murna.

    Idan mun daraja Allah

    Za mu so junanmu sosai.

(Ka kuma duba Far. 29:18; M. Wa. 4:​9, 10; 1 Kor. 13:8.)