Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 130

Mu Rika Gafartawa

Mu Rika Gafartawa

(Zabura 86:5)

  1. 1. Ubanmu mai ƙauna

    Ya aiko da Yesu fa,

    Domin ya yafe zunubi,

    Ya cire mutuwa ma.

    Idan mun yi tuban gaske,

    Zai yafe zunubanmu.

    Allah zai gafarta mana

    Don fansar Yesu Kristi.

  2. 2. Allahnmu Jehobah

    Zai nuna mana jinƙai

    In mun koyi halayensa

    Na yafe wa mutane.

    Nuna tausayi ga kowa

    Da kuma yin haƙuri,

    Mu riƙa girmama juna,

    Mu ƙaunaci junanmu.

  3. 3. Ya dace dukanmu

    Mu riƙa nuna jinƙai.

    Domin kar mu riƙe juna

    A cikin zuciyarmu.

    In mun yi koyi da Allah

    Wanda shi mai ƙauna ne,

    Za mu riƙa nuna jinƙai

    Kamar Mahaliccinmu.

(Ka kuma duba Mat. 6:12; Afis. 4:32; Kol. 3:13.)