Me Ya Sa Mutane Ke Mutuwa?
Amsar Littafi Mai Tsarki
Idan muka yi rashin wani, yana da sauki mu soma tunanin abin da ya sa mutane ke mutuwa. Littafi Mai Tsarki ya ce: “Karin mutuwa zunubi ne.”—1 Korintiyawa 15:56.
Me ya sa dukan mutane suke zunubi kuma suke mutuwa?
Mutane na farko, Adamu da Hawwa’u sun mutu saboda sun yi zunubi ga Allah. (Farawa 3:17-19) Mutuwa ce kawai sakamakon tawayen da suka yi wa Allah, domin a gare shi ne “mabulbular rai ta ke.”—Zabura 36:9; Farawa 2:17.
Dukan zuriyar Adamu sun sami illar zunubin da ya yi. Littafi Mai Tsarki ya ce: “Zunubi ya shigo cikin duniya ta wurin mutum daya, mutuwa kuwa ta wurin zunubi; har fa mutuwa ta bi kan dukan mutane, da yake duka sun yi zunubi.” (Romawa 5:12) Dukan mutane suna mutuwa domin sun yi zunubi.—Romawa 3:23.
Yadda za a kawar da mutuwa
Allah ya yi alkawarin cewa zai “haɗiye mutuwa har abada.” (Ishaya 25:8) Kafin a kawar da mutuwa, dole ne a cire tushenta, wato zunubi. Allah zai yi wannan ta wurin Yesu Kristi, wanda ‘ya dauke zunubin duniya!’—Yohanna 1:29; 1 Yohanna 1:7.